Atiku yace jam'iyar APC bata cinma burin ta ba kuma tana dab da samun cikas
Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya sauya sheka daga jam'iyar APC.
Atiku yayi murabus daga jam'iyar APC yace jam'iyar bata cinma burin ta ba kuma tana dab da samun cikas
A wata takarda da ya sa hannu ranar juma'a 24 ga watan nuwamba, tsohon mataimakin shugaban kasa wanda ya kasance tamkar jigo a jam'iyar APC ya nuna bacin ran sa ga yanda gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari bata jawo matasa ba cikin tawagar sa.
karanta Yan Nijeriya baza su sake zaben PDP - inji jam'iyar APC
Atiku yayi iki'rari cewa jam'iyar APC bata biya bukatun jama'a da suka yi alkawarin biya kuma bata neman membobin jam'iyar domin neman shawara ko kafin ta aikata ayyukan ta.
Wannan sabon al'amarin ya faru bayan wata bidiyo da tayi yawo a duniyar gizo inda Tsohon mataimakin shugaban kasa ke bayyana anniyar sa na zaben 2019
Atiku Abubakar ya sauya sheka zuwa jam'iyar APC cikin watan febreru na 2014 daga jam'iyar adawa ta PDP inda ya samu damar zama mataimakin shugaban kasa Olusegun Obasanjo daga 1999 zuwa 2007.
A bisa takardar da ya fitar tsohon mataimakin shugaban kasa yace bayan ya nemi shawarar daga Allah da iyalen sa da magoya bayan sa ya yanke hukunci yin murabus daga jam'iyar APC kana zai yi nazari kafin ya sanar da sabuwar akidar sa.
from pulse.ng - Nigeria's entertainment & lifestyle platform online
0 Comments
Feel free to drop a comments to help us serve you better
Your Opinion matters a lot to Us
Disclaimer Comments expressed here do not reflect the opinions of lexxytechcorporations.blogspot.com or any employee thereof