Farfesa Aisha Madawaki malama ce a fannin ilimin halayen dan adam a nan jami'ar Usman Danfodio dake jihar Sokoto
Gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya rantsar da mace ta farko da ta zama farfesa a fadin jihar a matsayin kwamishna tare da wasu.
Farfesa Aisha Madawaki malama ce a fannin ilimin halayen dan adam a nan jami'ar Usman Danfodio dake jihar.
An rantsar da ita a matsayin kwamishnar ilimi tare da Ahmed Barade Wamakko da Garba Yakubu Tsitse da Bello Isa Ambarura a matsayin kwamishnoni ranar talata 16 ga watan janairu 2018.
Duk a cikin sabon rantsarwa da gwamnan yayi akwai tsohon dan majalisar wakilai Umar Bature da tsohon shugaban makarantar kimiya ta jihar dakta Bello Rabiu Alkali wadanda aka nada a matsayin masu baiwa gwamnan shawara akan ayyuka ta musamman tare da Alhaji Bello Buba wanda aka ratsar a matsayin sabon shugaban karamar hukumar Wamakko.
A jawabin shi a bikin rantsuwa da aka gudanar a gidan gwamnati jihar, gwamna Tambuwal ya shawarci sabbin kwamishnonin da su amfani da wannan damar wajen biyan bukatar al'ummar jihar da samad da cigaba a jihar.
Tambuwal yace gwamnatin shi na kan tafarkin inganta rayuwar al'ummar jihar ta hanyar aiwatar da ayyukan cigaba.
from pulse.ng - Nigeria's entertainment & lifestyle platform online
0 Comments
Feel free to drop a comments to help us serve you better
Your Opinion matters a lot to Us
Disclaimer Comments expressed here do not reflect the opinions of lexxytechcorporations.blogspot.com or any employee thereof